Gwamnatin Burkina Faso ta nuna gamsuwa da yadda dangantakarta da Türkiye ke kara karfi, tana mai cewa hadin gwiwar kasashen biyu na ci gaba da bunkasa a fannoni da dama. Ministan harkokin wajen kasar, Karamoko Jean Marie Traoré, ya bayyana hakan yayin ganawarsa da jakadiyar Türkiye a kasar.
A ganawar da aka yi a ranar Talata, wadda ta hada da wasu jami’ai daga bangarorin biyu, an tattauna nasarorin da aka samu a fannoni kamar tsaro, ilimi, sufuri na jiragen sama, kiwon lafiya da kuma hulda ta majalisa. Wadannan nasarori sun samo asali ne daga yawan ziyarce-ziyarcen jami’an kasashen biyu da ake yi lokaci zuwa lokaci.
Haka kuma, bangarorin sun tattauna muhimman batutuwa na gaba, ciki har da taron diflomasiyya na Antalya, shirya taron kasuwanci tsakanin ‘yan kasuwa na kasashen biyu, da kuma wata tawagar likitoci da ake sa ran za ta kai ziyara domin ayyukan jinya.
Ministan ya karfafa a ci gaba da musayar ziyara tsakanin kasashen domin kara dankon zumunci da fadada hadin gwiwa. A cewarsa, wannan alaka na da matukar muhimmanci wajen bunkasa ci gaba da fahimtar juna tsakanin Burkina Faso da Türkiye.














