Amurka za ta bi diddigin shafukan soshiyal midiya na shekara 5 na ‘yan Nijeriya masu son biza

Wannan ce doka ta baya-bayan nan da gwamnatin Donald Trump ta yi a yunƙurinta na ƙara tsaurara dokokinta na shige da fice, inda akasari aka fi saka ido kan Afirka.

Newstimehub

Newstimehub

18 Aug, 2025

055fb5f7d1dbb021798ed59b6af54a6dae8ca19b34ab0bb3a9effc3e6af89ef9

Amurka ta sanar da sabon tsarin biza ga ‘yan Nijeriya, inda ake bukatar duk masu neman biza su bayyana sunayen da suke amfani da su a shafukan sada zumunta na tsawon shekara biyar domin bincike a kansu.

‘‘Rashin bayar da bayanan kafafen sada zumunta na iya haifar da kin amincewa da bayar da biza da kuma rashin cancanta don samun biza a nan gaba,’’ in ji Ofishin Jakadancin Amurka a Nijeriya a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa X a ranar Litinin.

Ya ƙara da cewa masu neman bizar ‘‘ana bukatar su lissafa duk sunayen da suke amfani da su a shafukansu na sada zumunta da suka yi amfani da su cikin shekaru 5 da suka gabata a fom ɗin neman biza na DS-160.’’

Gwamnatin Nijeriya har yanzu ba ta mayar da martani kan wannan sabon tsarin bizar na Amurka ba.

Wannan umarnin ya zo ne a yayin da Amurka ke ƙara tsaurara dokokin biza da kuma ƙaƙaba takunkumin tafiya ƙasashe daban-daban na duniya, musamman ƙasashen Afirka.

A watan Yuli, Nijeriya ta buƙaci gwamnatin Trump ta sake duba wata doka da ta taƙaita wa’adin biza na wucin gadi ga ‘yan Nijeriya zuwa watanni uku kacal. Wannan umarni ya kuma shafi Kamaru da Habasha.