MDD ta yi gargadi kan yunwa a yankin Kordofan na Sudan a yayin da fararen-hula ke ƙara shiga matsi

Ƙungiyoyin bayar da agaji sun yi gargaɗi dangane da yadda yunwa ke ƙara ƙaruwa a Sudan da kuma matsalolin da suka shafi taƙaita zirga-zirga da kuma ƙaruwar rikice-rikice.
5 Dec, 2025
Hukumar Kwastam ta Jamhuriyar Nijar ta ƙwace nakiya 8,567

Aikin kamen, wanda Laftanar Kanal Fatimata Salifou Marafa, shugabar ofishin ta jagoranta, ya daƙile shigar da miyagun ababen fashewa cikin Nijar, lamarin da ya taƙaita isar irin waɗannan makamai ga ‘yanbindiga da ƙungiyoyin masu aikata laifuka.
4 Dec, 2025
Masu shiga tsakani na ECOWAS sun gana da shugabannin riƙon ƙwarya na Guinea-Bissau

A ranar Alhamis ne ƙungiyar ECOWAS ta dakatar da Guinea-Bissau daga hukumominta da ke yanke shawara bayan juyin mulkin sojojin wanda ya hambarar da Shugaba Umaro Sissoco Embalo.
3 Dec, 2025
Ghana na shirin gina tashar makamashin nukiliyarta ta farko

Ghana tana shirin fara shiga harkar makamashin nukiliya inda take niyyar fara gina tashar nukuliyarta ta farko daga shekarar 2027 domin faɗaɗa hanyoyin samun makamashi a ƙasar.
3 Dec, 2025

Kasashen Afirka sun fara yi wa mutane allurar rigakafin cutar HIV

Gwamnatin Sudan ta ce a shirye take ta yi aiki da MDD domin samar da zaman lafiya a ƙasar

Matsalar man fetur a Mali ta ragu bayan sojoji sun yi wa tankokin mai rakiya a ƙasar

Kungiyar RSF ta Sudan ta kashe daraktan kamfanin dillancin labarai a Al Fasher

Shugaban Guinea-Bissau ya tsere zuwa Senegal bayan sojoji sun yi masa juyin mulki
26 Nov, 2025
An ji ƙarar harbe-harbe a kusa da fadar shugaban ƙasar Guinea-Bissau- Rahotanni
Tun da fari hukumar zabe ta gargaɗi masu zaɓe, da ‘yan takara, da jam’iyyun siyasa, da ƙungiyoyin zaɓe da kuma kafofin watsa labarai game da sanar da yin taka tsan-tsan wajen sanar da duk wani sakamako.

26 Nov, 2025
Hukumomi a Nijar sun kama CFA fiye da miliyan 1.7 da dubban miyagun ƙwayoyi a jihar Tahoua
Jami’ai sun ƙwato FCFA miliyan 1.7, da kuma dubban kwayoyi na Tramadol, Farin Malam, da Diazepam, tare da wiwi, babura, da wayoyi.

24 Nov, 2025
“‘Yan’uwa ‘yan Sudan” suna son Turkiyya ta sa hannu a ƙoƙarin samar da zaman lafiya: Erdogan
Shugaban Turkiyya Tayyip Erdogan ya bayyana ranar Lahadi cewa “’yan uwa ‘yan Sudan ” suna son Turkiyya ta sa hannu a a ƙoƙarin samar da zaman lafiya a ƙasar da kuma yakin da ake yi.

24 Nov, 2025
Burhan ya yi watsi da tayin Amurka na tsagaita a Sudan, ya ce shi ne ‘mafi muni a tarihi’
A cikin wani bidiyo da sojoji suka saki a daren Lahadi, Janar Burhan ya ce bai yarda da tayin ba, ya zargi masu shiga tsakani da nuna son kai a ƙoƙarinsu na kawo ƙarshen yaƙin na Sudan.

22 Nov, 2025
Yaƙin Sudan: Fiye da yara 20 sun mutu sakamakon tsananin rashin abinci a cikin wata guda
Mutuwar yara 23 a yankin Kordofan ta nuna yadda ake da matuƙar buƙatar kayan jinƙai a ƙasar da ke arewa maso gabashin Afirka, inda yunwa ke ƙaruwa bayan fiye da watanni 30 na yaki.

22 Nov, 2025
An ƙaddamar da taron shugabannin ƙasashen G20 a Afirka ta Kudu
A yayin wannan taron wanda jigonsa zai kasance ‘hadin kai, daidaito da ɗorewa’, shi ne taron G20 na farko da aka taba gudanarwa a nahiyar Afrika, kuma zai mayar da hankali kan sassauta bashi ga ƙasashe masu ƙaramin ƙarfi.

20 Nov, 2025
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Kafofin watsa labarai na cikin gida sun ce jirgin yana ɗauke da kimanin mutum 120, kuma daga cikinsu kimanin 50 kawai aka iya cetowa kawo yanzu.

18 Nov, 2025
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
Ranar Alhamis ne dai majalisar dokokin ƙasar ta amince da sunan alƙalin da shugaban ƙasar ya miƙa mata a matsayin sabon alƙalin alƙalan ƙasar.

17 Nov, 2025
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Bayanai daga masana’natar mai sun nuna cewa za a kara farashin mai kama daga kashi 1.18 cikin 100 zuwa kashi 3.54 cikin 100, inda za a sayar da ko wace lita ɗaya ta mai kan kuɗi GH¢13.15 (wato naira 1731.90 kuɗin Nijeriya).

17 Nov, 2025
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
Wata gada ta rufta a wata mahaƙar ma’adinai na kobolt a kudu maso gabashin Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo inda ta kashe aƙalla masu haƙar ma’adinai 32, kamar yadda wani jami’in gwamnati a yankin ya bayyana ranar Lahadi.


