An ƙaddamar da taron shugabannin ƙasashen G20 a Afirka ta Kudu

A yayin wannan taron wanda jigonsa zai kasance ‘hadin kai, daidaito da ɗorewa’, shi ne taron G20 na farko da aka taba gudanarwa a nahiyar Afrika, kuma zai mayar da hankali kan sassauta bashi ga ƙasashe masu ƙaramin ƙarfi.
22 Nov, 2025
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC

Kafofin watsa labarai na cikin gida sun ce jirgin yana ɗauke da kimanin mutum 120, kuma daga cikinsu kimanin 50 kawai aka iya cetowa kawo yanzu.
20 Nov, 2025
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki

Ranar Alhamis ne dai majalisar dokokin ƙasar ta amince da sunan alƙalin da shugaban ƙasar ya miƙa mata a matsayin sabon alƙalin alƙalan ƙasar.
18 Nov, 2025
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana

Bayanai daga masana’natar mai sun nuna cewa za a kara farashin mai kama daga kashi 1.18 cikin 100 zuwa kashi 3.54 cikin 100, inda za a sayar da ko wace lita ɗaya ta mai kan kuɗi GH¢13.15 (wato naira 1731.90 kuɗin Nijeriya).
17 Nov, 2025

Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC

An samu rahotanni 32 na yi wa ‘yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher – Likitoci

Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na ‘yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya

AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder

MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
14 Nov, 2025
An gabatar da GH¢302bn matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Kamfanin dillancin labaran ƙasar Ghana ya ambato ministan yana cewa “adadin kuɗin da gwamnatin za ta kashe a shekarar zai kasance cedi biliyan 302.5.”

13 Nov, 2025
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Bayan mayaƙan RSF sun ƙwace Al Fasher, sun mayar da hankali wurin yin arangama da sojojin Sudan a wasu sabbin wurare.

13 Nov, 2025
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Tun da fari a sanarwar da ta fitar, Rundunar Tsaro ta Ghana, GAF ta ce mutum shida ne suka mutu a wajen jarabawar neman aikin da aka yi ranar Laraba, 11 ga watan Nuwamban 2025.

13 Nov, 2025
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Ministocin ƙasashen ƙungiyar G7 sun bayyana goyon bayansu ga yunƙurin diflomasiyya na neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan, inda suka yi kira ga masu ruwa da tsaki na ƙasashen waje su goyi bayan yunƙurin.

11 Nov, 2025
Gwamnatin Trump ‘ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5’ don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Kuɗin da aka biya daga wani asusun tallafin cirani da gudun hijira zai kasance karo na farko na tura kuɗi tsakanin gwamnati zuwa gwamnati daga asusun, in ji sanatan.

11 Nov, 2025
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Daraktan WHO na yankin Afirka, Dr Mohamed Janabi a wani sako na Ranar Ciwon Siga ta Duniya ya ce nahiyar tana ganin ta’azzarar cutar sikari saboda tsarin yanayin rayuwa mara kyau da karuwar mummunar kiba da teba da kuma rashin tsarin kiwon lafiya mai

11 Nov, 2025
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Ƙasashen da suka yi Allah wadai da RSF sun haɗa da Canada, Sifaniya, Birtaniya, Norway, Jamus, Ireland, Sweden, Austria, Croatia, Jamhuriyar Czech, Finland, Poland da Switzerland.

10 Nov, 2025
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
Birnin El Obeid ya karɓi sama da mutum 175,000 da aka raba da muhallansu daga jihohi uku na yankin Kordofan cikin watan da ya gabata.

9 Nov, 2025
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin ‘ɓoye laifukan yaƙi’: Likitocin Sudan
Ƙungiyar Likitocin Sudan ta ce: “RSF ta tattara ɗaruruwan gawawwaki daga tituna da unguwannin birnin, suka binne wasu cikin kabarun bai-ɗaya sannan kuma suka ƙone wasu a wani yunƙurin ɓoye shaidar laifukan da suka aikata wa fararen-hula.”

8 Nov, 2025
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Sojojin sun kakkaɓo jirgi maras matuƙin samfarin ƙasar China a lokacin da yake wucewa ta saman birnin inda rahotanni suka ce jirgin ya nufi yammacin El-Obeid domin kai hari kan wuraren soja da na farar-hula



