ECOWAS ta yi Allah wadai da yunƙurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin

ECOWAS ta ce za ta ci gaba da mara wa Benin baya ta dukkan hanyoyin da suka dace ciki har da yiwuwar tura sojojinta na ko-ta-kwana na yanki don kare ikon kasar da tsarin mulkin ta.
7 Dec, 2025
Fadar Shugaban Benin ta ce har yanzu Patrice Talon ne a kan mulki

Jami’an sojoji a Benin ranar Lahadi sun sanar cewa sun rushe Shugaban Kasa Patrice Talon, ko da haka cibiyarsa ta ce shi ya tsira kuma sojoji suna dawo da tsarin mulki.
7 Dec, 2025
Sojojin Benin sun yi ikirarin juyin mulki a Jamhuriyar Benin

Gungun na sojin waɗanda suke kiran kansu, ‘Military Committee for Refoundation’ wato Kwamitin Soja na Sake Gina Ƙasa’, sun sanar da cire shugaban ƙasa mai ci Patrice Talon.
7 Dec, 2025
Shugaba Mahama ya yaba wa Amurka kan cire harajin da ta sa kan kayayyakin gona na Ghana

Shugaban Ghana ya ce kayayyakin gona na Ghana waɗanda ake kaiwa Amurka da suka haɗa da koko, avokado, lemu, barkono, albasa da doya, a yanzu ba za a rinƙa saka musu haraji ba.
6 Dec, 2025

Yara 43 na cikin fararen hula 79 da RSF ta kashe a harin jirage marasa matuƙa a Kordofan ta Kudu

Burkina Faso ta saki ma’aikatan agajin da ta kama kan zargin ‘leƙen asiri’

MDD ta yi gargadi kan yunwa a yankin Kordofan na Sudan a yayin da fararen-hula ke ƙara shiga matsi

Hukumar Kwastam ta Jamhuriyar Nijar ta ƙwace nakiya 8,567

Masu shiga tsakani na ECOWAS sun gana da shugabannin riƙon ƙwarya na Guinea-Bissau
3 Dec, 2025
Ghana na shirin gina tashar makamashin nukiliyarta ta farko
Ghana tana shirin fara shiga harkar makamashin nukiliya inda take niyyar fara gina tashar nukuliyarta ta farko daga shekarar 2027 domin faɗaɗa hanyoyin samun makamashi a ƙasar.

1 Dec, 2025
Kasashen Afirka sun fara yi wa mutane allurar rigakafin cutar HIV
Allurar Lenacapavir, wadda ake yin ta sau biyu a shekara, tana rage haɗarin yaɗa HIV fiye da kashi 99.9 cikin 100, wanda hakan a aikace yake sanya ta zama rigakafi mai ƙarfi.

30 Nov, 2025
Gwamnatin Sudan ta ce a shirye take ta yi aiki da MDD domin samar da zaman lafiya a ƙasar
Gwamnatin Sudan ta bayyana cewa a shirye take ta yi aiki kafaɗa da kafaɗa da Majalisar Ɗinkin Duniya domin samar da zaman lafiya da tsaro a ƙasar da kuma isar da kayayyakin agaji ga mabuƙata.

29 Nov, 2025
Matsalar man fetur a Mali ta ragu bayan sojoji sun yi wa tankokin mai rakiya a ƙasar
Tun daga watan Satumba, ‘yan ta’adda daga wata ƙungiya da ke da alaƙa da Al-Qaeda suka toshe hanyoyin jigilar mai zuwa wasu birane, lamarin da ya raunana tattalin arzikin ƙasar da ke Yammacin Afirka.

29 Nov, 2025
Kungiyar RSF ta Sudan ta kashe daraktan kamfanin dillancin labarai a Al Fasher
Ministan watsa labaran Sudan ya ce dakarun RSF ne suka kashe Taj Al-Sir Ahmed Suleiman a cikin gidansa tare da ɗan uwansa

28 Nov, 2025
Shugaban Guinea-Bissau ya tsere zuwa Senegal bayan sojoji sun yi masa juyin mulki
Senegal ta tabbatar da isar Shugaba Embalo Dakar “cikin ƙoshin lafiya ” bayan juyin mulki ya hana fitar da sakamakon zaɓe a Guinea-Bissau.

26 Nov, 2025
An ji ƙarar harbe-harbe a kusa da fadar shugaban ƙasar Guinea-Bissau- Rahotanni
Tun da fari hukumar zabe ta gargaɗi masu zaɓe, da ‘yan takara, da jam’iyyun siyasa, da ƙungiyoyin zaɓe da kuma kafofin watsa labarai game da sanar da yin taka tsan-tsan wajen sanar da duk wani sakamako.

26 Nov, 2025
Hukumomi a Nijar sun kama CFA fiye da miliyan 1.7 da dubban miyagun ƙwayoyi a jihar Tahoua
Jami’ai sun ƙwato FCFA miliyan 1.7, da kuma dubban kwayoyi na Tramadol, Farin Malam, da Diazepam, tare da wiwi, babura, da wayoyi.

24 Nov, 2025
“‘Yan’uwa ‘yan Sudan” suna son Turkiyya ta sa hannu a ƙoƙarin samar da zaman lafiya: Erdogan
Shugaban Turkiyya Tayyip Erdogan ya bayyana ranar Lahadi cewa “’yan uwa ‘yan Sudan ” suna son Turkiyya ta sa hannu a a ƙoƙarin samar da zaman lafiya a ƙasar da kuma yakin da ake yi.

24 Nov, 2025
Burhan ya yi watsi da tayin Amurka na tsagaita a Sudan, ya ce shi ne ‘mafi muni a tarihi’
A cikin wani bidiyo da sojoji suka saki a daren Lahadi, Janar Burhan ya ce bai yarda da tayin ba, ya zargi masu shiga tsakani da nuna son kai a ƙoƙarinsu na kawo ƙarshen yaƙin na Sudan.



