Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da Kwamitin Shura kan harkokin addini da zamantakewa

Majalisar ta ƙunshi mambobi 67 waɗanda aka zaɓo daga faɗin ƙananan hukumomi 44 na jihar Kano.

Newstimehub

Newstimehub

10 Sep, 2025

f2206c3ff35c380412657f2e7e9f8213e84394d1bbd4a26f8359c8958a4fcf40

Gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da Majalisar Shura, a matsayin wani sabon kwamiti don jagoranta da ba da shawarwari kan al’amuran da suka addini da zamantakewa da ke shafar ‘yan jihar.

Da yake jawabi a yayin bikin kaddamarwar a gidan gwamnati, Gwamnan ya bayyana majalisar a matsayin wani muhimmin ginshiki na kokarin gwamnatinsa na tabbatar da adalci, gaskiya, da haɗin kai a harkokin mulki.

A cewarsa, Majalisar Shura za ta taka muhimmiyar rawa wajen bayar da shawarwari kan harkokin addini da na jama’a tare da tabbatar da cewa ana jin muryoyin ‘yan kasa wajen yanke shawara.

“Manufar wannan gwamnati ita ce tabbatar da cewa mutane sun shiga cikin harkokin mulki. Muna son ‘yan jiharmu su ba da gudunmawar ra’ayoyinsu da shawarwari don ci gaban jihar baki daya.”