Shugaba Erdogan ya jinjina wa Jaruman Turkiyya a Ranar Nasara

Shugaba Erdogan a cikin saƙonsa na ranar Asabar, ya bayyana wannan rana a matsayin alamar imani mai ƙarfi na ‘yan ƙasar, ruhin jarumtaka, da kuma haɗin kai wajen yaƙi don ‘yanci da cin gashin kai.

Newstimehub

Newstimehub

31 Aug, 2025

ca35c5c0f7e45c926e5c68d0f81308065885cfc8b69201a08179fc114b080169

Shugaba Recep Tayyip Erdogan na Turkiyya ya fitar da saƙo a ranar 30 ga Agusta, yana tunawa da Ranar Nasara, wani muhimmin lokaci a tarihin Turkiyya.

Erdogan, a cikin saƙonsa na ranar Asabar, ya bayyana wannan rana a matsayin alamar imani mai ƙarfi na ‘yan ƙasar, ruhin jarumtaka, da kuma haɗin kai wajen yaƙi don ‘yanci da cin gashin kai.

“Babbar Nasara, wanda aka samu ta hanyar ƙaunar ƙasa daga sojojinmu masu jaruntaka da haɗin kai na al’ummarmu, ya karya sarƙoƙin bauta kuma ya buɗe hanya zuwa ga cin gashin kanmu,” in ji Erdogan.

Ya jaddada cewa Ranar Nasara ba wai kawai nasarar soja ba ce, amma kuma tana nufin “farfaɗowa” na al’ummar Turkiyya da gwagwarmayarta don wanzuwa da cin gashin kai na har abada.

A ƙarƙashin jagorancin uba wurin kafa Jamhuriyar Turkiyya, Mustafa Kemal Ataturk, yakin soja wanda ya kasance wani ɓangare na Babban Hari, ya fara a ranar 26 ga Agustan 1922, ya tabbatar da cin gashin kan Turkiyya kuma aka kammala shi a ranar 18 ga Satumba na shekarar da ta biyo baya.

Masana tarihi sun jaddada cewa nasarar, wadda Ataturk ya jagoranta wurin samu, ta bayyana ƙudurin Turkiyya na mulkin kai da kuma kasancewarta mai ɗorewa a Anatolia.