Gwamnatin Nijar ta ƙwace mahaƙar zinari daga kamfanin Australia

Gwamnatocin mulkin soji na Jamhuriyar Nijar da maƙotansu Burkina Faso da Mali sun matsa lamba kan kamfanonin haƙar ma’adanai na ƙasashen waje a shekarun baya bayan na, inda Nijar ta ƙwace kamfanin haƙar yuraniyom na Faransa, Orano a watan Yuni.

Newstimehub

Newstimehub

9 Aug, 2025

2024 07 06t181513z 154699585 rc2pp8amniuc rtrmadp 3 westafrica security sahel 1

Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar ta sanar da ƙwace mahaƙar zinari ɗaya tilo a ƙasar, bayan da ta zargi kamfanin Australia da ke gudanar da ita da “manyan laifukan keta doka” a yayin da gwamnatin take neman karɓe ragamar harkokin ma’adanai na ƙasar.

Gwamnatin soji, wadda ta ƙwace mulki daga gwamnatin farar-hula a shekarar 2023, ta sha alwashin magance rashin tsaro da ya addabi ƙsar.